Isa ga babban shafi
CAF-Libya

Libya ta nemi hurumin daukar nauyin gasar Afrika a 2017

Kasar Libya ta fara tura bukatar ta zuwa ga hukumar Kwallon Afrika CAF domin karbar bakuncin gasar cin kofin Afrika a 2017. Bayan an ba Afrika ta kudu huruminta na daukar nauyin gasar a a bana.

Tambarin Hukumar CAF da ke kula da Kwallon kafa a Nahiyar Afrika
Tambarin Hukumar CAF da ke kula da Kwallon kafa a Nahiyar Afrika
Talla

Kasar Libya ce dai ya kamata ta dauki gasar cin kofin Afrika da aka kammala a bana a kasar Afrika ta kudu amma saboda rikicin kasar da ya yi sanadiyar kawo karshen mulkin Kanal Gaddafi aka ba kasar Afrika ta kudu damar daukar nauyin gasar.

Mataimakin Firimiyn Libya Awad al-Baraassi, ya ce suna fatar daukar nauyin gudanar gasar domin wasannin su zo dai dai da lokacin bukin cika shekaru 60 da samun ‘yancin kai.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.