Isa ga babban shafi
Najeriya

An saki yara 876 da ake tsare dasu a Najeriya

A Najeriya hukumar UNICEF ta tattauna da hukumomin tsaron kasar, hakan ya kai ga sakin yara 876, da aka jima ana tsare da su a wasu barikokin sojin kasar, bisa zarginsu da alaka da kungiyar Boko Haram.

Rundunar sojin Najeriya a baya ta tsare yara da take zargin suna da alaka da Boko Haram.
Rundunar sojin Najeriya a baya ta tsare yara da take zargin suna da alaka da Boko Haram. © RFI/Ben Shemang
Talla

Darakatan hukumar ta UNICEF na yakunan yammaci da kuma tsakiyar Africa, Manuel Fontain, ya ce a baya Yaran su 876, suna zaune ne a yankunan da mayakan Boko Haram suka taba mamayewa.

A baya dai rundunar sojin Najeriya ta saki da yawa daga cikin yaran da take tsare da su bayan kammala bincike a kansu.

Amma a gefe guda hukumar ta UNICEF ta ce mai yiwuwa ne akwai wasu yaran da dama da ake tsare da su wasu barikokin sojin Najeriya da ke arewa maso gabashin kasar.

Har yanzu ba'a bayyana tsawon lokacin da yaran suka shafe a tsare ba, zalika ba'a bayyana ajin shekarunsu ba.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.