Najeriya
Kotun Majistare a Najeriya ta sallami masu fafutukan kafuwar Biafra 35
A Nigeria wata kotun Majistare dake Fatakwal ta sallai wasu mutane 35 dake tsare saboda fafutukan neman kasar Biafra daga Najeriya.
Wallafawa ranar:
Talla
Kamfanin Dillancin labaran Nigeria, NAN na cewa mutanen na tsare ne tun ranar 20 ga watan Janairu na wannan shekara a lokacin da suke zanga-zangan nuna farin cikinsu da nasarar zaben Donald Trump na Amurka wanda suke ganin zai taimaka a sami kasar Biafra daga Najeriya.
Alkalin Kotun Andrew Jaja a lokacin da yake sallaman mutanen ya ce sun kwashe kwanaki 37 a tsare ba tareda wasu kwararan hujjoji ba daga masu bincike.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu