Isa ga babban shafi
Najeriya

Najeriya: Yawan wadanda suka rasu sakamakon cutar Sankarau ya karu

Mai’aikatar lafiya ta Najeriya, ta ce yawan wadanda suka rasa rayukansu a dalilin barkewar cutar sankarau a sassan kasar ya karu 328, daga cikin mutane 2,524 da suka kamu da cutar.

Daya daga cikin yara da ke karbar allurar rigakafi ta cutar Sankarau
Daya daga cikin yara da ke karbar allurar rigakafi ta cutar Sankarau meningvax.org
Talla

Daraktan yada labaran ma’aikatar lafiyar, Boade Akinola ya ce alkalummansu na nuni da cewa kananan hukumomi 90 annobar ta shafa a johohi 16 da ke Najeriya, Jihohin sun hada da Kano, Katsina, Zamfara, Kebbi, Niger, Abuja, Osun, Cross Rivers, da kuma Legas.

Sauran jihohin da cutar a bulla sun hada da Nasarawa, Taraba, Jigawa, Filato, Yobe, Sakwato da kuma Niger.

Zalika ma’aikatar lafiyar ta ce, annobar ba ta tsaya kawai a Najeriya ba, cutar ta sankarau ta bulla a kasashen Niger, Chadi, Kamaru, Togo da kuma Burkina Faso.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.