Isa ga babban shafi
Najeriya

Watanni 9 ba a biyan malaman makaranta a Bayelsa

Malaman Makarantu a Jihar Bayelsa da ke Najeriya sun kaddamar da wani yajin aikin gama gari, saboda abinda suka kira kin biyan su albashi na watanni tara da rabi.

Gwamnan Jihar Bayelsa Seriake Dickson
Gwamnan Jihar Bayelsa Seriake Dickson Wordpress.com
Talla

Malaman sun ki amincewa da tayin da Gwamnatin Jihar ta yi musu na karbar albashin wata guda dan kaucewa yajin aikin.

Shugaban kungiyar malaman, Kalama Toinpre ya ce zasu ci gaba da kauracewa azuzuwa sai Gwamnatin Jihar ta biya su akalla albashin watanni uku.

Toinpre ya kuma bukaci malaman da su gudanar da azumi da addu’oi na kwanaki 7 dan samun taimakon Ubangiji.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.