Najeriya
Boko Haram ta yi wa ‘yan gudun hijira ‘yankar Rago
An Gudanar da jana’izar wasu ‘yan gudun hijira 4 da mayakan Boko Haram suka yiwa yankar rago a Dalori da ke Jihar Barnon Najeriya.
Wallafawa ranar:
Talla
Rahotanni sun ce ‘yan gudun hijirar 4 da aka yanka suna zama a sansanin Dalori ne, kuma sun ci karo da mayakan ne lokacin da suke farauta a daji.
Mayakan Boko Haram na ci gaba da kai hare hare a wasu sassan Jihar Borno duk da nasarar da sojojin Najeriya suka samu na tarwatsa su.
Ko a makonnin ba ya sai da suka yiwa wasu manoma yankar rago a dai-dai lokacin da suke gudanar da ayyukan gonanakin su a kauyen Maiduguri.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu