Isa ga babban shafi
Najeriya

Najeriya: Jami'an tsaro sun hallaka 'yan bindiga 14 a Legas

Gamayyar jami’an tsaro da suka hada da ‘yan sanda da sojin ruwa a birnin Lagos a kudancin Najeriya, sun samu nasarar hallaka ‘yan bindiga 14 daga cikin wadanda suka kutsa kai cikin wata makaranta a Igbonla, Epe da ke birnin na Lagos tare da sace wasu dalibai kanana guda 6, a ranar Alhamis din da ta gabata.

Ramin da 'yan bindiga suka yi a jikin katangar makarantar Sakandaren Egbonla Epe da ke birnin Legas, inda suka sace dalibai shida.
Ramin da 'yan bindiga suka yi a jikin katangar makarantar Sakandaren Egbonla Epe da ke birnin Legas, inda suka sace dalibai shida. naijagists
Talla

An dai sace yaran ne daga wuraren kwanansu da misalin karfe 6 na safiyar ranar ta Alhamis.

Kafin sace yaran dai, sau uku, ‘yan bindigar suna hankoron idda nufinsu, wanda basu cimma nasara ba, sakamakon jami;an da aka girke suna tsaron makarantar.

Daga bisani ne suka huda katangar makaranta ta baya, inda suka yi amfani da shi wajen awon gaba da yaran.

Rahotanni sun ce gamayyar jami’an tsaron na cigaba da dannawa cikin jejin da ‘yan bindigar suka boye yaran domin ceto su, kuma a kokarin haka ne suka samu nasarar hallaka 14 daga ciki tare da kuma raunata wasu da dama.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.