Najeriya
Dan Majalisar wakilai ya tsallake rijiya da baya a Najeriya
Wani Dan Majalisar wakilan Najeriya daga Jihar Kano, Garba Durbunde, ya tsallake rijiya da baya, sakamakon kama shi da masu garkuwa da mutane suka yi akan hanyar Abuja zuwa Kaduna.
Wallafawa ranar:
Talla
Rahotanni sun ce, wasu daga cikin abokan aikin sa daga Yankin Arewa maso gabas suka biya diyyar naira miliyan 6 kafin a sako shi.
Garkuwa da mutane dan karbar kudi na kokarin sama ruwan dare a Najeriya.
Yanzu haka a Jihar Lagos, 'Yan Sanda na farautar wasu da suka sace daliban wata makaranta, kuma suka bukaci biyan su diyyar naira miliyan 400.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu