Dakta Aliyu Usman Tilde kan salon yaki da rashawa a Najeriya
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:27
Ga alama wasu ‘yan Najeriya sun fara dawowa daga rakiyar yaki da cin hanci da rashawa da gwamnatin kasar ke yi, ganin yadda kotuna ke ci gaba da wanke mutanen da ake zargi da rub da ciki da kudaden talakawa.
A kasa da wata guda, kotuna sun wanke alkalan da aka zargi da tara dukiya ta hanyar da basu kamata ba, kana a jiya wasu kotunan sun wanke shugaban Majalisar Dattawa Bukola Saraki da Godsday Orubebe da wata karamar kotu ta samu da laifi. Dakta Aliyu Usman Tilde, mai sharhi ne kan al’amuran yau da kullum a Najeriya ya yi mana tsokaci a tattaunawarsu da Bashir Ibrahim Idris.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu