Isa ga babban shafi
Najeriya

Mata 'Yan Kunar Bakin Wake Sun Kashe Mutane 12 a Borno

A Najeriya wasu ‘yan mata biyar ‘yan kunar bakin wake sun tasar da bama-bamai inda suka kashe mutane 12 da jikkata wasu 11 a jihar Borno

Wani hari da kungiyar Boko Haram ta kai wa ayarin motocin dakon mai a garin Maiduguri kwanan baya
Wani hari da kungiyar Boko Haram ta kai wa ayarin motocin dakon mai a garin Maiduguri kwanan baya STRINGER / AFP
Talla

‘Yan Sandan sun gaskata wadannan alkaluma inda suka ce suna ci gaba da gudanar da bincike sosai.

Babu wata kungiyar da ta fito fili ta ce ita ta tura ‘yan matan da jigidan bama-bama, amma kuma an saba ganin ‘yan kungiyar Boko Haram na wannan aiki.

Kakakin Rundunar ‘yan sandan Borno Victor Isuku ya fadi cewa an kai wannan hari ne Lahadi da yamma a kauyen Kofa mai nisan kilomita takwas daga birnin Maiduguri.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.