Isa ga babban shafi
Najeriya

Najeriya ta yi karin girma ga sojoji dubu 6

Rundunar sojin Najeriya ta yi wa sojoji dubu 6 da 199 karin girma sakamakon rawar da suka taka a yaki da kungiyar Boko Haram musamman a yankin arewa maso gabashin kasar, in da rikicin ya fi kazanta.

Wasu daga cikin sojojin Kamaru da ke yaki da Boko Haram a arewa maso gabashin Najeriya
Wasu daga cikin sojojin Kamaru da ke yaki da Boko Haram a arewa maso gabashin Najeriya AFP PHOTO/HO/NIGERIAN ARMY
Talla

Wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, Sani Usman ya fitar, ta ce, shugaban sojin kasar, Laftanar Janar Tukur Buratai ya rattaba hannu don amince wa da karin girmar a wannan Talata.

Sanarwar ta ce, sojojin da aka yi wa karin girmar mabanbanta, na aiki ne a karkashin rundunar Operation Lafiya Dole.

Sanarwar ta bayyana adadin sojojin da sabbin mukamansu kamar haka haka:

1.Sitaf Saje -Warant Ofisa –329.
2. Saje -Sitaf Saje –371.
3. Kofur -Saje –707.
4. Las-Kofur – Kofur –1,290.
5. Firaivet – Las- kofur –3,502.

Rundunar sojin Najeriya ta bukaci sojojin da su kara kaimni wajen yaki da Boko Haram, wadda tun a shekarar 2009, sojojin ke fafutukar kawo karshenta.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.