Isa ga babban shafi
Najeriya

Biafra: Rundunar 'yan sandan Najeriya ta tura karin jami'ai kudancin kasar

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta kara yawan jami’anta a yankunan Kudu maso gabashi da kuma Kudu maso Kudancin kasar, domin murkushe duk wata barazanar tada zaune tsaye daga bangaren masu fafutukar neman kafa kasar Biafra, wadanda suka sha alwashin hana gudanar da zaben kujerar gwamnan Jihar Anambra.

Wasu 'yan kungiyar IPOB masu ra'ayin kafa kasar Biafra
Wasu 'yan kungiyar IPOB masu ra'ayin kafa kasar Biafra naijagists.com
Talla

Zalika wasu majiyoyin daga hukumomin tsaron kasar, sun ce, rundunar ‘yan sandan na sanya idanu kan shugaban masu fafutukar ta kafa Biafra, wato Nmandi Kanu, domin dakile duk wani yunkuri da zai iya yi, na neman tserewa daga kasar, idan kotu ta amsa bukatar gwamnatin Najeriya, na janye belinsa, domin sake kama shi.

Gwamnatin Najeriya na zargin Nnamdi Kanu, da saba sharuddan da aka gindaya mishi na bada beli, kan haka ne kuma ta bukaci babbar kotun tarayya da ke Abuja ta soke belin, ta kuma bai wa jami’an tsaro damar sake damke shi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.