Isa ga babban shafi
Najeriya

Rundunar sojin Najeriya ta kare dalilin harbin gargadi a Umuahia

Rundunar sojin Najeriya tayi bayani kan dalilin da ya sa jami’anta suka yi harbin gargadi a garin Umuahia.

Jagoran masu neman kafa Biafra Nnamdi Kanu, a harabar babbar kotun Najeriya, da ke garin Abuja. Ranar 10 ga Janairu 2017.
Jagoran masu neman kafa Biafra Nnamdi Kanu, a harabar babbar kotun Najeriya, da ke garin Abuja. Ranar 10 ga Janairu 2017. REUTERS/Stringer
Talla

Sanarwar sojin mai dauke da sanya hannun Manjo Oyegoke Gbadamosi, tace wasu matasa ne suka jefi tawagar sojojin dake ratsa garin, inda suka raunata soja guda da kuma wata mata dake wucewa, abinda ya sa sojojin suka yi harbin gargadi, amma babu wanda ya rasa rai.

Tun a makon jiya mazauna yankin kudu maso gabashin Najeriya ke korafi kan jibge sojojin.

Kamar yadda daya daga cikin mazauna jiohin da ke yankin Mazi Obinna Okparuba ya bayyana, yayinda yake zantawa da sashin Hausa na RFI, inda ya ce babu bukatar hakan tunda babu wani tashin hankali a yankin.

01:01

Rundunar sojin Najeriya ta bayyana dalilin harbin gargadi a Umuahia

Bashir Ibrahim Idris

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.