Ba za mu janye dakarunmu ba daga Abia- Rundunar Najeriya
Rundunar sojin Najeriya ta bayyana cewa za ta ci gaba da gudanar da aikinta a karkashin shirin Operation Python Dance da aka kaddamar don magance miyagun ayyuka a yankin kudu maso gabashin kasar.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Rundunar ta bukaci 'yan Najeriya da su yi watsi da sanarwar da gwamnan jihar Abia Okezie Ikpeazu ya fitar, wadda ke nuna cewa, za ta janye dakarunta da ake aiki a karkashin shirin Operation Python Dance II.
Mai Magana da yawun rundunar sojin, Birgediya Janar Sani Usman Kuka Sheka, ya ce, babu kamshin gaskiya a game da janye dakarunsu.
A ranar Alhamis da ta gabata ne, gwamna Ikpeazu ya ce, rundunar za ta fara janye sojojin daga titunan unguwannin jihar Abia a yau Jumma’a.
Za a ci gaba da gudanar da shirin har zuwa karshen shekara kamar yadda Sheka ya tabbatar.
Shirin ya kunshi yaki da masu garkuwa da mutane da fashi da makami da kashe-kashe da kuma yaki da miyagun ayyukan masu kokarin raba kan kasa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu