Sojin Najeriya zasu fadada atasaye zuwa Kudu maso yammacin kasar
Rundunar sojin Najeriya ta ce zata kaddamar da fara atasayen da ta yi wa lakabi da "Operation Crocodile Smile", wato murmushin kada a Hausance, kuma atasayen sojin zai gudana ne a yankin Kudu maso kudancin kasar da kuma wasu daga cikin yankunan kudu maso yammaci.
Wallafawa ranar:
Kakakin rundunar sojin Najeriya, Birgediya Janar Sani Usman Kuka Sheka, ya sanar da haka a ranar Asabar din data gabata.
Birgediya Janar sani Usman ya ce, bai kamata a rika sako siyasa cikin atsayen da sojin Najeriyar ke yi a sassan kasar ba, musamman ma kan wanda suka kaddamar a yankin kudu maso gabashin kasar, inda masu fafutukar kafa Biafra suka yi yunkurin tada yamutsi.
A cewar kakakin idan ba’a manta ba, a farkon shekarar da muke ciki, rundunar sojin ta gudanar da atasayen da ta yiwa lakabi da "Operation Harbin Kunama" a yankunan Arewa maso yammacin kasar da kuma arewa ta tsakiya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu