Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Dr Aliyu Musa kan fara shara'ar 'yan Boko Haram a Najeriya
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:28
Ministan Shari'a na Najeriya, Abubakar Malami, ya ce daga ranar 9 ga watan gobe za’a fara sauraron shariar ‘ya'yan kungiyar Boko Haram 1,600 da ake tsare da su a sassan kasar, saboda ayyukan ta’addanci. Ministan ya ce akwai masu shigar da kara da aka wakilta su gabatar da kararrakin, yayinda hukumar kare wadanda ake tuhuma suka gabatar da jerin lauyoyi da za su wakilci masu bukata. Garba Aliyu Zaria ya tattauna da Dr Aliyu Musa Manpa na sashen Mulki da Siyasa na Jamiar Maiduguri.