Isa ga babban shafi
Najeriya

An kammala jigilar Alhazan Najeriya daga Saudiya

Hukumar kula da aikin Hajji ta Najeriya, NAHCON ta kammala jigilar ‘yan kasar daga Saudiya da suka yi aikin hajjin bana.

Wasu daga cikin Alhazan Najeriya da suka yi aikin hajjin bana a Saudiya
Wasu daga cikin Alhazan Najeriya da suka yi aikin hajjin bana a Saudiya dailytrust
Talla

A wannan Litinin ne jirgin Max Airline mai lamba NGL 2110 ya kwaso tawagar karshe daga filin jiragen sama na King Abdulaziz da ke birnin Jeddah.

Jirgin wanda zai sauka a Kano bayan yada zango a birnin Fatakwal, ya taso daga Saudiya ne da misalin karfe 6:53 na safe agogon Najeriya.

NAHCON ta ce, akwai Alhazan Kano 172 da kuma Alhazan jihar Rivers 76 a cikin jirgin, sai kuma ma'aikata 30.

Tun a ranar 7 ga watan Satumban da ya gabata ne aka fara jigilar dawo da Alhazan Najeriya gida bayan kammala aikin hajjin bana.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.