Najeriya
PDP ta bukaci a tsige shugaba Buhari
Jam’iyyar adawa at PDP a Najeriya ta bukaci tsige shugaban kasa Muhammadu Buhari saboda abinda ta kira korar Sakataren Gwamnati Babacir Lawal da shugaban hukumar leken asiri Ayo Oke.
Wallafawa ranar:
Talla
Kakakin Jam’iyyar Ayo Adeyeye ya zargi shugaban da nuna ban-banci wajen yaki da cin-hancin, inda ya ke cewa marasa galihu sai a hada su da EFCC ko ICPC, masu galihu kuma ayi musu bincike da hukuncin cikin gida.
Adeyeye ya ce wannan nuna ban-bancin da Buhari ke nunawa 'yan Najeriya wani laifi ne da ya dace a tsige shi daga kujerar sa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu