Najeriya
Najeriya na son ta san 'yanmatan da suka mutu a hanyarsu ta zuwa Turai
Gwamnatin Najeriya ta bukaci Majalisar Dinkin Duniya da ta gudanar da bincike a kan abinda ya yi sanadiyar mutuwar wasu 'yanmatan kasar guda 26, wadanda ake zargin sun mutu lokacin da suke kokarin tsallakawa zuwa nahiyar Turai.
Wallafawa ranar:
Talla
Kungiyar da ke yaki da safarar mutane ta kasar (NAPTIP) ce ta bayyana bukatar, tare kuma da neman sanin wadanda ke da jirgin da ya dauke 'yanmatan da kuma dalilin mutuwar su.
Ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ya ce 'yanmatan da suka mutu din suna da shekaru tsakanin 14 zuwa 18.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu