Plateau - Ana zaman zullumi a Riyom
Mai Magana da yawun gwamnan jihar Filato Dan Manjang ya ce mutane na zaman zullumi a yankin da aka kai harin
Wallafawa ranar:
Manjang ya ce daga cikin matasan yankin wasu sun yi kokarin yin zanga-zanga, amma an shawo kan su.
A cewarsa, mutane sun fara zargin jami’an tsaro da hannu a cikin kashe-kashen da ake yi a yankin, domin har zuwa yanzu an kasa kama wadanda ke kawo wadannan hare-hare.
Amma jami’in ya ce yana iya yiwuwa rikicin na da nasaba da siyasa, musamman ganin cewa zaben kananan hukumomi ya karato.
Rahotanni daga jihar ta Filato sun ce akalla mutane 9 aka tabbatar da mutuwar su lokacin da wasu yan bindiga suka kai hari a karamar hukumar Riyom lokacin mutane ke komawa gida bayan sun ci kasuwa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu