Isa ga babban shafi
Najeriya

Najeriya ta sa hannu kan Kwangilar gina tashar lantarki a Mambilla

Gwamnatin Najeriya ta sanya hannu kan kwangilar fara aikin gina tashar samar wutar lantarki ta Mambilla da ke jihar Taraba, wadda zata samar karfin wutar megawatts dubu 3,050, bayan shafe shekaru akalla 40 ana kokarin tabbatar da shirin.

Ministan lura da bunkasa fannin makamshi, ayyuka da samar da gidaje na Najeriya Baba Tunde Fashola.
Ministan lura da bunkasa fannin makamshi, ayyuka da samar da gidaje na Najeriya Baba Tunde Fashola. REUTERS/Akintunde Akinleye
Talla

A ranar Juma’ar da ta gabata ne Ministan bunkasa makamshi, ayyuka da samar da gidaje na Najeriya Baba Tunde Fashola, ya sanya hannu kan takardar yarjejeniyar fara aikin hadin gwiwar da wasu kamfanonin kasar China.

Ginin tashar lantarkin da za’a shafe shekaru 6 kafin kammala shi, zai lashe dala biliyan 5 da miliyan 800, wato naira triliyan 2.1 kenan.

Bankin Exim na China ne zai samar da dala biliyan 4.9 yayinda gwamnatin Najeriya zata bada kashi 15, wato dala miliyan 868.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.