An kara daukar matakan tsaro a Numan - SP Abubakar
Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa, ta tabbatar da mutuwar jami’anta hudu a musayar wuta da suka yi, da wasu ‘yan bindiga a karamar hukumar Numan.
Wallafawa ranar:
Kakakin rundunar SP Usman Abubakar, ya ce har yanzu basu kai ga gano, ku su waye ‘yan bindigar ba.
Harin ya jefa tsoro cikin zukatan mazauna yankin, lamarin da ya tilastawa da dama tserewa zuwa wasu wuraren, don kaucewa abinda zai iya biyo baya.
SP Abubakar ya ce babu gaskiya cikin jita-jitar cewa ‘yan bindigar Fulani ne da suke kokarin daukar fansa bisa kashe musu mata da kanan yara da aka yi a watan da ya gabata, bincike ne kawai zai tabbatar da ko su wayen maharan.
Kakakin ‘yan sandan, ya kuma bukaci jama’a da su kwantar da hankulansu, kasancewar an kara yawan jami’an tsaro a karamar hukumar domin tabbatar da doka da oda.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu