PDP na neman afuwar 'yan Najeriya- Atiku
Tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar ya bayyana Jam’iyyar PDP a matsayin sabuwa, in da ya bukaci ‘yan Najeriya su yi mu su afuwa kan kura-kuran da suka tafka a matsayinsu na ‘yan Adam.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
A yayin zantawarsa da sashen Hausa na RFI, Atiku wanda ya koma PDP a ‘yan kwanakin da suka gabata bayan ya raba gari da APC mai mulki ya ce, sun kama hanyar kawo gyara a PDP bayan zaben sabbin shugabannin jam'iyyar a karshen mako.
Muryar Abubakar Atiku kan neman afuwar 'yan Najeriya
A wani sako da ya aike ta kafar twitter, Atiku ya ce lokaci ya yi da ya kamata PDP ta hada kai don ganin cewa ta karbe ragamar tafiyar da Najeriya.
Atiku Abubakar tare da tsohon shugaban Najeriya Goodluck Jonathan a wurin taron jam'iyyar PDP
It’s good to be back home. pic.twitter.com/w2KzaVfS8Z
Atiku Abubakar (@atiku) December 10, 2017
A shekarar 2015 ne jam’iyyar APC ta kwace mulki daga hanun PDP wadda ta yi mulki tsawon shekaru 16 bayan karawar da aka yi tsakanin shugaba Muhammadu Buhari da Goodluck Jonathan.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu