Isa ga babban shafi
Najeriya

Sojin Najeriya sun kame mayakan Boko Haram 167

Jami’an sojin Najeriya da ke karkashin rundunar musamman ta Operation Lafiya Dole, sun samu nasarar kame mayakan Boko Haram, 167.

Wasu daga cikin jami'an sojin Najeriya a garin Baga da ke wajen birnin Maiduguri. 13 ga watan Mayu, 2013.
Wasu daga cikin jami'an sojin Najeriya a garin Baga da ke wajen birnin Maiduguri. 13 ga watan Mayu, 2013. REUTERS/Tim Cocks
Talla

Cikin sanarwar da ya sa wa hannu, Kanal Onyema Nwachukwu, mataimakin daraktan hulda da jama’a na rundunar ta musamman, ya ce an samu nasarar ce, bayan sabunta kai wa mayakan na Boko Haram farmaki a yankunan da ke zagaye da tafkin Chadi, makwanni 2 da suka gabata zuwa yanzu.

Sojin Najeriyar sun kuma ceto mata 67, da yara 173 daga hannun mayakan.

Wani lokaci nan gaba ake sa ran mika fararen hular zuwa hukumomin da ke lura da sansanonin ‘yan gudun hijira da ke arewa maso gabashin kasar, bayan an kammala tantance su.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.