Bakonmu a Yau
Malam Aminu Umar kan sabon faifan bidiyon jagoran mayakan Boko Haram Abubakar Shekau
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:08
‘Yan Najeriya suna ci gaba da tofa albarkacin baki, kan sabon faifan bidiyon da shugaban kangiyar Boko Haram Abubakar Shekau ya fitar, inda yake daukar nauyin hare haren baya-bayan nan da aka kai a lokutan bukukuwan sabuwar shekara a jihar Borno dake arewa maso gabashin Najeriya. Shekau ya bayyana ne a cikin yanayi na rashin karsashi ba kamar yadda aka saba ganinsa a baya ba. To ko menene ra’ayin masu sharhi kan sha’anin tsaro a kasar dangane da wannan sabuwar fitowa ta shekau. A tattaunawarsa da Mahaman Salisu Hamisu, Malam Aminu Umar na Kwalejin fasaha dake Kaduna a Najeriya ya yi tsokaci a kai.