Isa ga babban shafi
Najeriya

Najeriya: Tashar ruwa ta kan Tudu zata samar da dubban ayyukan yi

Akalla ayyukan yi da ba zasu gaza dubu biyar ba, ake sa ran cewa tashar jirgin ruwa ta kan tudu, da Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya jagoranci kaddamar wa jihar Kaduna zata samar.

Tashar ruwa ta ka tudu da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya kaddamar, zata taimaka wajen kaddamar zata taimaka wajen saukakawa 'yan kasuwa a arewa maso yammacin kasar gudanar da harkokinsu.
Tashar ruwa ta ka tudu da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya kaddamar, zata taimaka wajen kaddamar zata taimaka wajen saukakawa 'yan kasuwa a arewa maso yammacin kasar gudanar da harkokinsu. BusinessDay
Talla

Tashar wadda ita ce irinta ta farko da aka kaddamar a Najeriya, za ta taka rawar gani wajen bunkasa tattalin arzikin kasar.

Shugaba Buhari ya ce, tashar ta Kaduna daya ce daga cikin tashoshin kan tudu guda bakwai da ake ginawa a sassan kasar.

Ana sa ran a zangon farko na fara aikinta, tashar zata iya daukar kayayyaki da yawansu ya kai ton dubu 29,000, baya ga samar da dubban ayyukan yi.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.