A daidai lokacin da sojojin Najeriya ke ci gaba da kokarin tabbatar da tsaro a yankin Arewa maso gabashin kasar mai fama da rikicin Boko Haram, babban abin da mazauna wannan yanki ke bukata shi ne samar da tsaro hatta a cikin yankunan karkara, wanda hakan zai bai wa jama’a damar gudanar da noma da kuma sauran harkokin kasuwanci. A cewar Alhaji Muhammadu Mustapha Maikanuri, wanda bai jima da kai ziyara a jihar Borno ba, a halin yanzu abu ne mai wuya jama’a su iya rayuwa a cikin yankunan karkara, saboda a cewarsa har yanzu akwai sauran ‘yan Boko Haram da ke yi wa rayukan jama’a barazana.
Sauran kashi-kashi
-
Arewa maso Yammacin Najeriya ne mafi hatsari saboda matsalar tsaro - Bincike
Kungiyar 'Global Rights' ta bayyana yankin arewa maso yammacin Najeriya a matsayin mafi hadari, saboda yadda 'yan bindiga ke kisa da take hakkin Bil Adama ba tare da kaukautawa ba.18/04/202403:16 -
Kuskure ne a yi tunanin ɗagawar darajar naira ba zai ɗore ba - Dakta Kurfi
Darajar Naira na cigaba da ɗagawa a Najeriya tare da saukar farashin wasu kayayyakin abinci a wasu kasuwannin ƙasar, abinda ya sa wasu tunanin cewar tasirin saukar Dalar ne ya sanya wasu kayayyakin suka fara sauka.17/04/202403:19 -
Tattaunawa da Sanata Ikira Aliyu Bilbis kan tsaro a jihar Zamfara
Hukumomi a Najeriya daga matakin jiha zuwa na kasar baki ɗaya na daukar matakai daban daban wajen samar da zaman lafiya a jihar Zamfara, amma har ya zuwa wannan lokaci ba'a kai ga cimma biyan bukata ba.16/04/202403:26 -
Yadda rayuwa ta kasance bayan da muka faɗa hannun mayakan Boko Haram - Maryama
A ranar Lahadi, 14 ga watan Afrilun nan aka cika shekaru 10 da sace dalibai mata na makarantar sakandaren Chibok sama da 250 da mayakan Boko Haram suka yi a jihar Borno.15/04/202403:17 -
Kwamred Bello Basi kan shirin gina hanyayoin zamani a Najeriya
Gwamnatin Najeriya ta sanar da kashe naira biliyan 4 kan kowacce kilomita ta hanyar zamani da ake ginawa daga jihar Legas zuwa birnin Kalaba.12/04/202403:40