Isa ga babban shafi
Najeriya

Babban Sifeton 'yan sandan Najeriya ya sha tambaya

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya gayyaci babban Sifeton ‘yan sandan Najeriya Ibrahim Idris zuwa ofishinsa, domin amsa tambayoyi kan dalilansa na kin bin umarnin komawa zuwa Benue domin kawo karshen kashe-kashen da suka auku a jihar.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari. REUTERS/Dan Kitwood
Talla

An shafe akalla mintuna 30, shugaba Buhari yana ganawa da babban Sifeton ‘yan sandan, wanda daga bisani ya fice daga fadar gwamnatin Najeriyar, ba tare da cewa komai ba.

Kakakin shugaban Najeriyar Malam Garba Shehu, ya tabbatar da ganawar sifeton ‘yan sandan da shugaban kasa, sai dai bai yi karin bayani akan ganawar ba.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya bayyana mamakin rashin bin umarninsa na komawa Benue, da babban Sifeton ‘yan sandan kasar ya yi, a lokacin da yake ganawa da masu ruwa da tsaki kan batun shawo kan matsalar Manoma da makiyaya a jihar Benue.

Wannan lamari yasa wasu daga cikin masu sharhi akan al'amuran yau da kullum, nazarin ko shugaban Najeriyar yana fuskantar kalubale na zagon kasa daga wasu daga cikin mukarrabansa akan fannonin tafiyar da kasar daban daban, ciki harda sha'anin tsaro da kuma tattalin arziki.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.