Najeriya
Sojan Najeriya sun kashe 'yan Boko Haram 5 da kubutar da mutane 149
Rundunar Sojan Najeriya ta sanar ta kashe mayakan kungiyar Boko Haram biyar da kubutar da wasu mutane 149 da aka yi garkuwa dasu a dajin Sambisa dake Arewa maso gabashin kasar.
Wallafawa ranar:
Talla
Onyeama Nwachukwu Mukaddashin kakakin Daraktan Hulda da jama’a na Rundunar Sojan Najeriya ya fadi cikin wata sanarwa cewa sun yi katarin kama ‘yan kungiyar Boko Haram din 5.
Ya sanar da cewa yanzu haka suna ta samun nasara a kokarin kakkabe sauran mayakan kungiyar Boko Haram dake hana sukuni a yankin Arewa maso gabashin kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu