Isa ga babban shafi
Najeriya

Babu tabbacin ranar dawowar Buhari daga London

Fadar shugaban Najeriya ta ce, ba za ta iya bada tabbaci ba kan cewar, shugaba Muhammadu Buhari zai koma gida daga birnin London a ranar Asabar mai zuwa kamar yadda aka tsara tun farko.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari tare da mukarrabansa
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari tare da mukarrabansa REUTERS/Tiksa Negeri/File Photo
Talla

Mai bai wa shugaban kasar shawara kan harkokin yada labarai, Femi Adesina ya bayyana haka a yayin zantawa ta wayar tarho da kafar talabijin ta Channels da ke kasar.

A farkon wannan makon ne shugaba Buhari ya koma birnin London don duba lafiyarsa, yayin da ake saran dawoarsa a ranar Asabar kafin kuma ya kai ziyara jihar Jigawa da ka arewacin Najeriya a ranar Litinin.

Kawo yanzu fadar shugaban ba ta bada bayani ba kan irin rashin lafiyar da Buhari ke fama da ita, lamarin da fadar ke cewa, wani al’amari ne da ya shafi rayuwar mutun.

A shekarar da ta gabata ne, shugaba Buhari mai shekaru 75 da haihuwa ya shafe tswon watanni hudu yana jinya birnin London.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.