Isa ga babban shafi
Najeriya

An kama wasu 'yan Boko Haram da suka sace daliban Chibok

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta kame wasu muhimman ‘yan kungiyar Boko Haram 22, da suka taka rawa wajen sace daliban makarantar ‘yan matan sakandiren Chibok 276 da ke jihar Borno a shekarar 2014.

'Yan kungiyar Boko Haram da suka taka rawa wajen sace 'yan matan sakandaren Chibok a shekarar 2014,  bayan shiga hannun jami'an tsaro a in Maiduguri. 18 ga watan Yuli, 2018.
'Yan kungiyar Boko Haram da suka taka rawa wajen sace 'yan matan sakandaren Chibok a shekarar 2014, bayan shiga hannun jami'an tsaro a in Maiduguri. 18 ga watan Yuli, 2018. REUTERS/Ahmed Kingimi
Talla

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Borno damian Chukwu, ya ce sun samu nasarar kame ‘yan Boko Haram din ne, bayan shirya dabaru sosai, tare da amfani da fasahohin zamani, a tsakanin 4 ga watan Yuli zuwa 9 ga watan na Yuli cikin wannan shekara ta 2018.

Wakilinmu Bilyaminu Yusuf ya aiko mana da rahoto akai.

01:33

An kama wasu 'yan Boko Haram da suka sace daliban Chibok

Bilyaminu Yusuf

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.