Magoya bayan Buhari sun saya masa takardar takara
Wata kungiyar magoya bayan shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ta saya masa takardar tsayawa takarar zabe akan Naira miliyan 45.
Wallafawa ranar:
Kungiyar mai suna 'Nigeria Consolidation Ambassadors Network' (NCAN) ta dauki matakin ne bayan sanarwar da aka fitar a hukumance da ke bayyana ranar da jam’iyyar APC mai mulki za ta gudanar da zaben fid da gwani da kuma farashin sayen takardar wato Form a turance.
Tuni aka mika takardar Chek na kudin ga shugaban Jam’iyyar APC ta kasa, Adams Oshiomole a birnin Abuja a ranar Laraba.
Ana sa ran shugaba Buhari ya samu tikitin wakiltar APC a takarar zaben 2019 mai zuwa, lura da cewa, babu wani fitaccen dan takara da ake ganin zai kalubalance shi wajen neman tikitin a karkashin inuwar Jam’iyyar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu