Isa ga babban shafi
Najeriya

Zaben fid da gwanin Lagos ya yi kyau- APC

Jamiyar APC mai mulkin Najeriya ta ce, ta gamsu da yadda aka gudanar da zabukan fitar da gwani a jihohin kasar, ciki kuwa har da jihar Lagos da gwamnanta mai ci, Akinwunmi Ambode ya gaza kai labari. Jam'iyyar ta ce tsarin da aka yi amfani da shi a  zaben, ya bai wa talakawa damar zaben wanda suke so ya mulke su ko ya wakilce su, ba wanda wasu kusoshin jam'iyya ke so ba.

Gwamna Akinwunmi Ambode ya sha kashi a hannun Babajide Sanwo-Olu a zaben fid da gwani
Gwamna Akinwunmi Ambode ya sha kashi a hannun Babajide Sanwo-Olu a zaben fid da gwani premiumtimes
Talla

Shugaban jam'iyyar na kasa, Adam Oshiomhole ya bayyana cewa, zaben da aka gudanar a jihar Legas ya yi kyau bayan da farko Kwamitin Zaben ya ce, bai gamsu da zaben ba, amma Oshiomhole ya tabbatar da ingancinsa.

Tuni shalkwatan APC a Lagos  ya sanar da sakamakon zaben, in da ya ce, Ambode ya samu kuri'u dubu 72 da 901, yayin da abokin hamayyarsa, Babajide Sanwo-Olu ya samu kuri'u dubu 970 da 850.

Latsa alamar sautin da ke kasa don sauraren hirar da RFI Hausa ta yi da Oshiomhole bayan gudanar da zaben.

03:05

Hira da Oshiomhole kan zaben fid da gwani

Sai dai shugaban ya ce, jamiyyar ta yi watsi da sakamakon zaben da bangarori biyu suka gunanar a jihar Imo, in da ya ce, za a nada sabon kwamatin da zai sake gudanar da zaben daga nan zuwa ranar Juma’a mai zuwa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.