Isa ga babban shafi
Najeriya

Zan mara wa Atiku baya a zaben 2019- Obasanjo

Tsohon shugaban Najeriya, Olusegun Obasanjo ya ce, ya sauya matsayinsa na rashin goyon bayan tsohon mataimakinsa, Atiku Abubakar a zaben 2019.

Tsohon shugaban Olusegun Obasanjo da tsohon mataimakinsa  Abubakar da wasu shugabannin addinai a Najeiya, Mathew Kukah da Sheik Ahmad Gumi
Tsohon shugaban Olusegun Obasanjo da tsohon mataimakinsa Abubakar da wasu shugabannin addinai a Najeiya, Mathew Kukah da Sheik Ahmad Gumi RFI/Hausa
Talla

Mr. Obasanjo ya bayyana haka ne bayan ziyarar da Atiku Abubakar da wasu jiga-jigan jam’iyyar PDP suka kai masa a gidansa da ke birnin Abeokuta.

Obasanjo ya ce, ya yi amanna cewa, Atiku ya daidaita kansa kuma a yanzu haka ya cancanci samun goyon bayansa a zaben kasar mai zuwa.

Tsohon shugaban na Najeriya ya taya murna ga Atiku game da nasarar da ya samu ta wakiltar jam’iyyar PDP a zaben shugaban kasa, in da zai fafata da shugaba Muhammadu Buhari na jam’iyyar APC.

A can baya dai, Obasanjo ya lashi takobin rashin mara wa Atiku baya wajen fafutukarsa ta ganin mafarkinsa na zama shugabban kasa ya zama gaske.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.