Najeriya na gaf da samun tikitin halartar gasar cin kofin Afrika
Najeriya ta samu nasarar karbe ragamar jagorancin rukuni na biyar da take ciki, a wasannin neman cancantar halartar gasar cin kofin kasashen nahiyar Afrika.
Wallafawa ranar:
Najeriya ta samu nasarar ce, bayan wasan da ta doke Libya da kwallaye 3-2.
Odion Ighalo da Ahmed Musa ne suka ci wa Najeriya kwallayen, wadanda Ighalo ya ci biyu daga ciki.
A wasan neman cancantar zagayen farko tsakanin kasashen biyu da aka buga a garin Uyo, Najeriya ta lallasa Libya ne da kwallye 4-0.
A halin yanzu Najeriya ke kan gaba a rukuni da take ciki na 5 da maki 9, sai kuma Afrika ta Kudu da maki 8.
Libya ke a matsayi na uku da maki 4, yayinda kasar Seychelles ke matsayin ta karshe da maki 1.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu