Ba ma goyon bayan wani dan takara a Najeriya- Amurka
Amurka ta ce, babu wani dan takara da take mara wa baya a zaben Najeriya na shekarar 2019, in da za a fafata tsakanin shugaban kasa mai ci Muhammadu Buhari na jam'iyyar APC da kuma Atiku Abubakar na jam'iyyar PDP.
Wallafawa ranar:
Jami’in da ke kula da harkokin siyasa a ofishin Jakadancin Amurka, Phillip Franz ya bayyana haka a yayin zantawa da manema labarai a jihar Katsina jim kadan da kammala ganawa da mahukuntan jihar.
Franz ya ce, abin da Amurka ke goyon baya shi ne tsare-tsaren gudanar da zaben, in da ya ce, suna matukar mutunta ‘yancin Najeriya.
A cewar jami’in, Amurka na goyon bayan gudanar da sahihin zabe cikin kwanciyar hankali, yayin da ya ce, a shirye suke su bada dukkanin gudunmawa don gaanin zaben ya gudana cikin lumana.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu