Isa ga babban shafi
Najeriya

An kama masu taimakawa 'yan bindigar Zamfara a Legas

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta yi nasarar damke wasu mutane 4 da ke sana’ar saida shanu a mayankar dabbobi da ke karamar hukumar Agege a jihar Legas, bisa zargin mutanen suna taimakawa wasu 'yan bindigar da ke kai hare-hare a jihar Zamfara.

Wasu Shanu mallakar Fulani makiyaya a jihar Kaduna, da ke arewa maso yammacin Najeriya.
Wasu Shanu mallakar Fulani makiyaya a jihar Kaduna, da ke arewa maso yammacin Najeriya. STEFAN HEUNIS/AFP/Getty Images
Talla

‘Yan sandan sun shaidawa manema labarai cewa, mutanen suna taimakawa ‘yan bindigar ne ta hanyar sayen Shanu da sauran dabbobi na sata da barayin ke satowa daga jihar ta Zamfara, da kuma wasu sassan arewacin Najeriya.

Binciken jami’an tsaron Najeriya ya kuma gano cewar, ‘yan bindigar suna amfani da kudaden shanun satar wajen sayen muggan makamai daga Libya, su kuma yi amfani da su wajen kai farmaki kan garuruwan Tsafe, Zurmi, Shinkafi, Maradun, Maru da Brinin-Magaji da ke jihar ta Zamfara.

Mutane hudun da aka kama a jihar at Legas, kamar yadda 'yan sanda suka bayyana, sun hada da Alawani Abubakar, Alhaji Ago Atine, Mohammed Shagari da kuma Bashiru Aliyu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.