Isa ga babban shafi
Najeriya

INEC ta dage zaben Najeriya zuwa makon gobe

Hukumar Zaben Najeriya ta sanar da dage zaben shugaban kasar da na ‘yan majalisun da aka shirya gudanarwa yau asabar zuwa makon gobe, saboda wasu matsalolin da suka sha kan ta.

Wani dan sandan Najeriya, tare da jami'in hukumar zaben kasar INEC yayin daukar kayan aikin zabe daga ofishin hukumar ta INEC da ke garin Yola a Adamawa zuwa wasu sassan jihar. 15/02/2019.
Wani dan sandan Najeriya, tare da jami'in hukumar zaben kasar INEC yayin daukar kayan aikin zabe daga ofishin hukumar ta INEC da ke garin Yola a Adamawa zuwa wasu sassan jihar. 15/02/2019. REUTERS/Nyancho NwaNri
Talla

Shugaban hukumar Farfesa Mahmood Yakub ya bayyana haka yayin ganawa da manema labarai cikin dare, inda ya bayyana fuskantar wasu matsalolin gudanar da ayyukan zaben, a matsayin wani bangare daga cikin dalilan da suka haddasa sauya ranar zaben zuwa gaba.

Farfesa Yakubu ya sanar da daukar matakin bayan taron da ya jagoranta tsakaninsa da masu ruwa da tsaki kan zaben na Najeriya, da kuma wasu wakilan masu sa ido kan zabukan na cikin gida na kasashen ketare, sai kuma manyan jami’an hukumar ta INEC.

A yanzu dai ya tabbata Zaben shugaban kasa da na ‘yan Majalisar Wakilai da Dattijan Najeriya zai gudana a ranar Asabar, 23 ga watan Fabarairu, a maimakon 16 ga Fabarairu da aka tsara da farko.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.