Isa ga babban shafi
Najeriya-Kaduna

Kajuru: 'Yan bindiga sun raba mutane dubu 3 da muhallansu

Shugaban karamar hukumar Kajuru da ke Jihar Kaduna, Mista Cafra Caino, ya ce akalla mutane dubu 3000 sun rasa muhallansu, sakamakon hare-haren ‘yan bindiga kan wasu yankuna da ke karamar hukumar.

Shugaban karamar hukumar Kajuru Cafra Caino a jihar Kaduna ya ce 'yan bindiga sun tilastawa mutane kimanin dubu 3000 barin muhallansu.
Shugaban karamar hukumar Kajuru Cafra Caino a jihar Kaduna ya ce 'yan bindiga sun tilastawa mutane kimanin dubu 3000 barin muhallansu. Daily Trust
Talla

Yayin ganawa da manema labarai a wannan Juma’a, Caino, ya bayyana samun nasarar tsara hanyoyin magance matsalar tsaro a karamar hukumar ta Kajuru, bayan taron hadin gwiwa, tsakanin Kabilun Adara, Hausawa, da kuma Fulani da ke zaune a yankin.

Shugaban karamar hukumar ta Kajuru ya kuma koka kan yadda masu yada labaran karya ta hanyar kafofin sadarwa na zamani, suka kara hargitsa yanayin zaman dar-dar da mafi akasarin al’ummar yankin ke ciki.

Caino ya kara da bayyana rashin kyawun layukan sadarwar waya da hanyoyi, a matsayin manyan matsalolin da ke zama kalubale wajen tabbatar da tsaro a karamar hukumar ta Kajuru.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.