Isa ga babban shafi
Najeriya

Nafisa Abdullahi ta soki Buhari kan kisan Zamfara

Fitacciyar jarumar fina-finan Kannywood na Hausa, Nafisa Abdullahi ta caccaki shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari saboda yadda ya yi gum da bakinsa game da kashe-kashen da ake yi wa al’umma a wasu kauyuka da ke jihar Zamfara.

Nafisa Abdullahi
Nafisa Abdullahi Kannywood
Talla

Jarumar ta soki shugaban ne biyo bayan sakon ta’aziya da ya aika ta shafin Twitter ga iyalan wani matashi, Johnson Kolade da jami’an ‘yan sanda suka kashe shi a birnin Lagos.

A martanin da ta mayar wa Buhari, Nafisa ta ce, “ ka yi magana game da daruruwa da dubban mutanen da ake kashewa a Zamfara da sauran sassan arewacin kasar kafin kisan da aka yi wa Kolade, ko kuma ka magance matsalar a lokaci guda."

Jarumar ta kara da cewa, shugaban na tsoron tsokokaci kan kashe-kashen da ake yi a arewa, amma ya yi magana game da kisan da ya faru a kudancin kasar a cewarta.

A sakon da ya aika, shugaba Buhari ya bai wa 'yan Najeriya tabbacin cewa, za a hukunta jami'an 'yan sanda biyu da suka harbe Kolade har lahira a jihar Lagos, yana mai nuna takaicinsa kan al'amarin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.