Isa ga babban shafi
Najeriya

Abba Yusuf na kalubalantar nasarar Ganduje a kotu

Jam’iyar PDP reshen jihar Kano ta shigar da karar APC a gaban kotu, in da take kalubalantar nasarar da Gwamnan Jihar Abdullahi Umar Ganduje ya samu a zaben da aka gudanar. Kwanaki 20 kenan da Hukumar Zaben Najeriya Mai Zaman Kanta, INEC ta ayyana Ganduje a matsayin wanda ya yi nasara.

Abdullahi Umar Ganduje da  Abba Kabir Yusuf
Abdullahi Umar Ganduje da Abba Kabir Yusuf dailypost
Talla

Takardar korafin da PDP ta rubuta wa kotun sauraren korafe-korafen zabe, na cewa, dan takaranta Abba Yuusf ne ya samu nasara a zaben da aka gudanar a ranar 9 ga watan Maris da ya gabata.

Kazalila jam’iyyar adawar na korafin cewa, Hukumar INEC ba ta gudanar da zaben cikin mutunta dokoki da kundin tsarin mulkin kasar ba.

A yayin zantawa da manema labarai, Abba Yususf ya ce, PDP ta samu mafi yawan kuri’u a kananan hukumomi 44 a zaben na ranar 9 ga watan Maris.

A cewar Yusuf, suna addu’ar  kotun za ta fayyace hakikanin wanda ya yi nasara a zaben.

Jam’iyyar ta PDP ta bayyana cewa, matakin ayyana zaben ranar 9 ga watan Maris a matsayin wanda bai kammala ba, wani yunkuri ne na samar wa APC hanyar magudin dawo da dan takaranta akan karagar mulki.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.