Isa ga babban shafi
Bakonmu a Yau

Farfesa Muhammad Kabir Isa sace kashi 66 na kasafin da Najeriya ke warewa fannin Ilimi

Wallafawa ranar:

Kungiyar da ke kokarin ganin an tabbatar da gaskiya wajen ayyukan gwamnati ta Transparency International ta yi zargin cewa kashi 66 na kasafin kudin da gwamnatocin Najeriya ke warewa bangaren ilimi daga Tarayya zuwa kananan hukumomi sace su ake yi.Kungiyar ta kuma bayyana wasu dalilai da ke yiwa harkar bada ilimi targade a Najeriya, da suka hada da cin hanci, rashin kwararrun malamai, rashin zama wurin aikin da malaman ke yi, da kuma lalata da mata domin basu cin jarabawa da karkata kudaden da ake warewa wajen inganta makarantun da kuma samar musu kayan aiki.Dangane da wannan rahoto, Bashir Ibrahim Idris tattauna da Farfesa Muhammad Kabir Isa, na Jami’ar Ahmadu Bello dake Zaria.

Wasu daliban makarantar Firamare da ke Hausari a kauyen Michika a arewa maso gabashin Najeriya. 12/6/2017.
Wasu daliban makarantar Firamare da ke Hausari a kauyen Michika a arewa maso gabashin Najeriya. 12/6/2017. REUTERS/Akintunde Akinleye
Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.