Farfesa Muhammad Kabir Isa sace kashi 66 na kasafin da Najeriya ke warewa fannin Ilimi
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:31
Kungiyar da ke kokarin ganin an tabbatar da gaskiya wajen ayyukan gwamnati ta Transparency International ta yi zargin cewa kashi 66 na kasafin kudin da gwamnatocin Najeriya ke warewa bangaren ilimi daga Tarayya zuwa kananan hukumomi sace su ake yi.Kungiyar ta kuma bayyana wasu dalilai da ke yiwa harkar bada ilimi targade a Najeriya, da suka hada da cin hanci, rashin kwararrun malamai, rashin zama wurin aikin da malaman ke yi, da kuma lalata da mata domin basu cin jarabawa da karkata kudaden da ake warewa wajen inganta makarantun da kuma samar musu kayan aiki.Dangane da wannan rahoto, Bashir Ibrahim Idris tattauna da Farfesa Muhammad Kabir Isa, na Jami’ar Ahmadu Bello dake Zaria.