Isa ga babban shafi
Najeriya

Sojoji sun kashe 'yan sandan Najeriya

Rundunar 'yan Sandan Najeriya ta zargi sojojin kasar da kashe jami’anta guda 3 da kuma raunana wasu da dama lokacin da suka kamo wani mai garkuwa da mutane akan hanyar Ibi zuwa Jalingo da ke Jihar Taraba.

Wasu dag cikin sojojin Najeriya
Wasu dag cikin sojojin Najeriya Pulse.ng
Talla

Kakakin 'yan Sandan kasar Frank Mba ya ce, lamarin ya faru ne lokacin da sojojin suka bude musu wuta duk da gabatar da shaidar da ke nuna cewa, su jami’an 'yan sanda ne da ke gudanar da aikinsu.

Sai dai kakakin sojin Kanar Sagir Musa ya ce, 'yan sandan sun ki tsayawa a wurin binciken da sojoji ke yi, kana su suka fara bude musu wuta kafin mayar da martini.

Kanar Sagir Musa ya ce, bangarorin biyu tattauna kan lamarin, inda suka amince da kafa kwamitin bincike a karkashin Mukaddashin Sufeto Janar domin gano abinda ya faru.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.