Isa ga babban shafi
Najeriya - Kaduna

Yan bindiga sun nemi kudin fansar daliban da suka sace

Gwamnatin jihar Kaduna a Najeriya, ta ce tana kan tattaunawa da ‘yan bindigar da suka sace dalibai mata 6 da malamansu 2 daga kwalejin Engravers dake karamar hukumar Chikun.

Gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufa'i
Gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufa'i The Nation
Talla

Yayin Karin bayani kan halin da ake ciki, gwamnan jihar ta Kaduna Malam Nasir El Rufa’I yace an soma tattaunawar ce, bayan da ‘yan bindigar suka bukaci biyansu kudin fansa kafin sakin daliban da kuma malaman nasu.

01:03

Gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufa'i kan sace dalibai 6 da malamai 2

Aminu Sani Sado

Duk da cewa Kaduna na daga cikin jihohin Najeriya dake fama da matsalolin tsaro a wasu yankuna, sace daliban da 'yan bindigar suka yi ya zama bakon abu.

Tun bayan sace daliban dai rundunar ‘yan sanda a jihar ta kaddamar da farautar Yan bindigar kamar yadda kakakinta Yakubu Sabo ta tabbatar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.