Yan bindiga sun nemi kudin fansar daliban da suka sace
Gwamnatin jihar Kaduna a Najeriya, ta ce tana kan tattaunawa da ‘yan bindigar da suka sace dalibai mata 6 da malamansu 2 daga kwalejin Engravers dake karamar hukumar Chikun.
Wallafawa ranar:
Yayin Karin bayani kan halin da ake ciki, gwamnan jihar ta Kaduna Malam Nasir El Rufa’I yace an soma tattaunawar ce, bayan da ‘yan bindigar suka bukaci biyansu kudin fansa kafin sakin daliban da kuma malaman nasu.
Gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufa'i kan sace dalibai 6 da malamai 2
Duk da cewa Kaduna na daga cikin jihohin Najeriya dake fama da matsalolin tsaro a wasu yankuna, sace daliban da 'yan bindigar suka yi ya zama bakon abu.
Tun bayan sace daliban dai rundunar ‘yan sanda a jihar ta kaddamar da farautar Yan bindigar kamar yadda kakakinta Yakubu Sabo ta tabbatar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu