Isa ga babban shafi
Najeriya

'Yan bindiga sun kashe mutane a Zamfara

Wasu ‘yan bindiga sun kashe mutane akalla 18 a kauyen Karaye da ke Karamar Hukumar Gummi ta jihar Zamfara da ke Najeriya kamar yadda hukumomi da mazauna yankin suka tabbatar.

'Yan bindigar sun kaddamar da harin cikin daren da ya gabata
'Yan bindigar sun kaddamar da harin cikin daren da ya gabata Jakarta Globe
Talla

Mazauana yankin sun bayyana harin a matsayin mafi muni da suka gani a cikin watannin baya-bayan nan, inda ‘yan bindigar suka kwashe tsawon sa’o’i hudu suna cin karansu babu babbaka ba tare da halartar jami’an tsaro ba.

Gwamnatin jihar ta bayyana harin a matsayin na ramuwar gayya sakamakon kisan da aka yi wa wasu daga cikin dangin ‘yan bindigar makwanni da suka shude a gunzumar Bardoki da ke Gummi.

A ranar 3 ga watan Nuwamba ne, ‘yan kato da gora suka kashe ‘yan bindga bakwai da suka tuba kamar yadda rahotanni ke cewa.

Jihar Zamfara ta yi fama da hare-haren ‘yan bindiga da suka kashe daruruwan mutane, yayin da Gwamnan Jihar, Bello Matawalle ya cimma yarjejeniyar tsagaita wuta da ‘yan bindigar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.