Isa ga babban shafi
Nijar

Faransa za ta taimaka wa Nijar wajen kafa sabuwar gwamnati

Shugaba Emmanuel Macron na Faransa ya ce babban aikin da ke gaban shugaban Nijar Mahammadou Issofou a halin yanzu shi ne gudanar da karɓaɓɓen zaɓe a shekara ta 2021.

Emmanuel Macron da Mahamadou Issoufou a lokacin zantawa da manema labaru a Niamey, 23 Decembre 2017.
Emmanuel Macron da Mahamadou Issoufou a lokacin zantawa da manema labaru a Niamey, 23 Decembre 2017. LUDOVIC MARIN / AFP
Talla

Macron wanda ya zanta da shugaban na Nijar a cigaban ziyarar da yake yi a ƙasar, ya ce gwamnatinsa za ta taimaka wa Nijar wajen tabbatuwar hakan ta hanyar inganta zaɓuka masu zuwa.

Ya ƙara da cewa ƙasar ta Nijar ba za ta ci gaba ba, matuƙar ba ta samar da tsaro da kuma ingantaccen tsari na mulkin demokraɗiyya ba.

Zaben shekara ta 2021 da ake sa ran gudanarwa a ƙasar zai kasance zakaran-gwajin-dafi, kasancewar ƙasar ba ta taɓa samun nasarar miƙa mulki daga gwamnatin farar hula zuwa wata ta farar hular ba.

Sauran ɓangarorin da Faransa din za ta taimaka wa Nijar sun haɗa da inganta tsaro da kuma ci gaban ƙasa, a cewar Macron.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.