Isa ga babban shafi
Nijar

'Yan fashi da makami a sun mika makamansu ga gwamnatin Nijar

Wasu 'yan fashi da makami a Jihar Agadez dake Jamhuriyar Nijar sun mika wa gwamnati tarin makamai dake hannun su a karkashin wani shiri na yi musu afuwa.

Ministan cikin gidan Jamhuriyar Nijar Mohamed Bazoum, yayin da ya kai ziyarar aiki zuwa yankin Diffa.
Ministan cikin gidan Jamhuriyar Nijar Mohamed Bazoum, yayin da ya kai ziyarar aiki zuwa yankin Diffa. REUTERS/Luc Gnago
Talla

Bakin mika makaman ya gudana ne a karkashin jagorancin Ministan cikin gida na Jamhuriyar ta Nijar Bazoum Mohammed.

Wannan dai shi ne karo na uku cikin kasa da shekara guda, da 'yan fashi da makami suke mika makamai ga hukumomin kasar.

Makaman sun hada da manyan bindigogi masu sarrafa kansu, makaman roka da kuma alburusai masu tarin yawa.

Mutane sama da 30 ne suka mika makaman ga gwamnati, tare da shan alwashin cewa zasu bai wa jami'an tsaron kasar gudunmawa wajen tabbatar da doka da oda.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.