Isa ga babban shafi
Nijar

'Yan bindiga sun hallaka jami'an tsaron Nijar

Wasu ‘yan bindiga sun kai hari tare da kashe jami’an tsaron jamhuriyar Nijar 3, tare da raunata guda daya, a kauyen Goube tazarar kilomita 40 da birnin Yamai fadar gwamnatin kasar.

Wasu jami'an tsaron Jamhuriyar Nijar yayin da suke sintiri.
Wasu jami'an tsaron Jamhuriyar Nijar yayin da suke sintiri. RFI
Talla

Lamarin dai ya faru ne a cikin daren Litinin zuwa wayewar garin jiya Talata, inda rahotanni suka ce maharan sun zo ne a kan babura, kafin daga bisani su doshi bangaren iyakar kasar ta Nijar da Mali.

Wannan ne dai shi ne karo na farko da ‘yan bindiga ke kai hari makamancin haka a gaf da kofar birnin na Yamai, bayan irinsa da suka kai kusan shekaru 2 da suka gabata, a wani gidan yarin Koutoukale da ake tsare da ‘yan ta’adda a cikinsa.

Alkassoum Abdurrahman na daga cikin masana tsaro da ke kallon harin na baya bayan nan a mtsayin babbar barazana ga Jamhuriyar Nijar, kamar yadda ya bayyana a zantawarsa da Sashin Hausa na RFI.

00:51

Muryar Alkassoum AbduRahman masanin tsaro, akan hallaka jami'an tsaron Jamhuriyar Nijar

Abdoulkarim Ibrahim

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.