Isa ga babban shafi
Nijar

Nijar ta yi wa majalisar ministocinta garanbawul

A Jamhuriyar Nijar an yi wa majalisar ministoci garambawul bayan da Ministan Harkokin Wajen kasar Ibrahim Yacouba ya yi marabus daga mukaminsa.

Shugaban Nijar Muhamadou Issoufou
Shugaban Nijar Muhamadou Issoufou ludovic MARIN / AFP
Talla

Sanarwar da kafafen yada labaran gwamnati suka fitar na cewa, tuni aka nada Kalla Hankurau a matsayin sabon Ministan Harkokin Waje, sai Mahamadou Salissou Habi a ma’aikatar sadarwa, yayin da aka nada Mohamed Samro a matsayin ma’aikatar ilmin sakandare.

Ga alama dai an tilasta wa Ministan Harkokin Wajen yin marabus ne, sakamakon yadda jam’iyyarsa ta fito fili ta bayyana rashin amincewa da sabuwar hukumar zaben da aka kafa a kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.