Nijar ta yi wa majalisar ministocinta garanbawul
A Jamhuriyar Nijar an yi wa majalisar ministoci garambawul bayan da Ministan Harkokin Wajen kasar Ibrahim Yacouba ya yi marabus daga mukaminsa.
Wallafawa ranar:
Sanarwar da kafafen yada labaran gwamnati suka fitar na cewa, tuni aka nada Kalla Hankurau a matsayin sabon Ministan Harkokin Waje, sai Mahamadou Salissou Habi a ma’aikatar sadarwa, yayin da aka nada Mohamed Samro a matsayin ma’aikatar ilmin sakandare.
Ga alama dai an tilasta wa Ministan Harkokin Wajen yin marabus ne, sakamakon yadda jam’iyyarsa ta fito fili ta bayyana rashin amincewa da sabuwar hukumar zaben da aka kafa a kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu