Al'ummar Filingue sun koka bisa hare-haren 'yan bindiga
A Jamhuriyar Nijar, shugabannin al’umma a yankin Kourfeye Filingue a cikin jihar Tillabery sun bukaci mahukuntan kasar da su dauki matakan gaggawa domin karshen kashe-kashe da ke faruwa a yankin.
Wallafawa ranar:
A cikin ‘yan kwanakin da suka gabata an samu asarar rayukan jama’a da dama sakamakon irin wadannan hare-hare.
Yayin da ayke yiwa Sashin Hausa ba RFI akan matsalar, Alhaji Ibrahim Barke Doka, daya daga cikin shugabannin al’umma a yankin na Kourfeye, ya zargi jami’an tsaro da nuna sakaci.
Barke ya kara da cewa a halin da ake ciki, jama’ar yankin da wannan matsala ta shafa suna cikin firgici, wanda ka iya hana manoma damar gudanar da ayyukansu, abinda ya bayyana a matsayin babbar barazana.
Al'ummar Filingue sun koka bisa hare-haren 'yan bindiga
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu