Isa ga babban shafi
Nijar

Al'ummar Filingue sun koka bisa hare-haren 'yan bindiga

A Jamhuriyar Nijar, shugabannin al’umma a yankin Kourfeye Filingue a cikin jihar Tillabery sun bukaci mahukuntan kasar da su dauki matakan gaggawa domin karshen kashe-kashe da ke faruwa a yankin.

Wasu jami'an sojin Jamhuriyar Nijar.
Wasu jami'an sojin Jamhuriyar Nijar. Reuters
Talla

A cikin ‘yan kwanakin da suka gabata an samu asarar rayukan jama’a da dama sakamakon irin wadannan hare-hare.

Yayin da ayke yiwa Sashin Hausa ba RFI akan matsalar, Alhaji Ibrahim Barke Doka, daya daga cikin shugabannin al’umma a yankin na Kourfeye, ya zargi jami’an tsaro da nuna sakaci.

Barke ya kara da cewa a halin da ake ciki, jama’ar yankin da wannan matsala ta shafa suna cikin firgici, wanda ka iya hana manoma damar gudanar da ayyukansu, abinda ya bayyana a matsayin babbar barazana.

01:07

Al'ummar Filingue sun koka bisa hare-haren 'yan bindiga

Abdoulkarim Ibrahim

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.